EPISODE · May 28, 2026 · 14 MIN
Kanun Labaran Hausa na 2026-05-28 (HausaRadio.net Headline news)
from Hausa Newsletter · host Hausa Radio News Headlines
Ƙarin bayani: https://hausadictionary.com/HausaRadio.net/2026-05-28== BBCHausa Safe 2026-05-28 ==Mai gabatarwa: Aisha Sharif Baba#1 🎧 @0:15 Amurka da Iran sun kai wa juna hare-hare a yankin Gabas ta Tsakiya, abin da ke neman illata ƙwaryar tsagaita wuta da aka cimma.#2 🎧 @0:24 Ƙarin hare-haren da Isra’ila ta kai sun faɗa ciki da kewen birnin Tyre da ke kudancin Lebanon, inda suka faɗa kan wani gini da ya kama da wuta daga bisani.#3 🎧 @0:34 A Najeriya, jam’iyyar hamayya ta ADC ta bayyana sakamakon zaɓen fidda gwani na shugaban ƙasa, inda ta ce tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ne ya samu nasara, sai dai wasu...#4 🎧 @1:04 Yankin Tafkin Chadi wuri ne mai albarkatun ruwa da aikin gona, amma rashin tsaro ya ci gaba da addabar al’ummar yankin.== BBCHausa Hantsi 2026-05-28 ==Mai gabatarwa: Aisha Sharif Baba#5 🎧 @2:02 Maimaicin labarin ƙarin hare-haren da Isra’ila ta kai ciki da kewen birnin Tyre da ke kudancin Lebanon.#6 🎧 @2:11 Gwamnatin Australia ta ce tana neman diyya ta kusan dala biliyan 1.5 daga katafaren kamfanin samar da kayayyakin amfani na Amurka 3M.#7 🎧 @2:19 A Najeriya, ƙungiyoyin Fulani makiyaya sun mayar da martani kan wani rahoton Amurka da ke cewa Fulani masu ɗauke da makamai na kai hare-hare kan gonakin Kiristoci da wuraren ibada.== BBCHausa Rana 2026-05-28 ==Mai gabatarwa: Aisha Aliyu Jafar#8 🎧 @3:37 Amurka ta zargi Iran da saɓa ƙa’idojin tsagaita wuta bayan da ta harba makamai zuwa Kuwait.#9 🎧 @3:47 Gobara ta yi ajalin ɗalibai goma sha shida a wata makarantar kwana ta mata da ke Kenya.#10 🎧 @3:59 A Najeriya, yayin da ayyukan daba ke ta’azzara a wasu sassan Arewa, musamman jihar Kano, wani babban ɗan siyasa ya shawarci ‘yan siyasa su daina bai wa matasa makamai da ƙwayoyi.#11 🎧 @4:20 Sakamakon da aka fitar na ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar ADC ya bar baya da ƙura, inda waɗanda suka yi rashin nasara suka yi fatali da sakamakon.#12 🎧 @4:52 Wata ƙungiyar Fulani ta ja hankali kan yadda take cewa jami’an tsaro na ƙura wa matasan Fulani ido yayin bukukuwan Sallah.== BBCHausa Yamma 2026-05-28 ==Mai gabatarwa: Aisha Aliyu Jafar#13 🎧 @5:44 Amurka ta ce ita da Iran sun amince da shirin yarjejeniyar da za ta tsawaita tsagaita wuta da suka cimma.#14 🎧 @5:55 Firaministan Isra’ila ya bai wa sojojin ƙasar umarnin faɗaɗa mamayarsu a Zirin Gaza.#15 🎧 @6:00 A Najeriya, ƙungiyar ƙwadago ta NLC ta koka kan yadda tattalin arziki da matsalar tsaro ke ƙara taɓarɓarewa a ƙasar.#16 🎧 @6:27 Har ila yau a Najeriya, yayin da ayyukan daba ke ƙara ta’azzara a wasu sassan Arewa, musamman Kano, wani babban ɗan siyasa ya ba takwarorinsa shawara su daina ɗaure wa matasa gindi.== DWHausa Safe 2026-05-28 ==Mai gabatarwa: Musa Tijjani Ahmad#17 🎧 @7:20 Rukunin farko na ‘yan ƙasar Ghana kusan ɗari uku da aka kwashe daga Afirka ta Kudu sakamakon sabbin hare-haren ƙyamar baki sun isa gida lafiya.#18 🎧 @7:31 A ƙasashen Afirka, a duk lokacin da layya ta kama, jama’a na fuskantar matsalar tsaftar muhalli saboda datti, ledoji da jini da ake barin su a kan tituna.#19 🎧 @7:43 Hedikwatar tsaron Najeriya ta bayyana samun nasarar kashe ‘yan ta’adda fiye da ɗari uku da sha bakwai.#20 🎧 @8:26 An yi musayar wuta tsakanin Amurka da Iran a kusa da Mashigar Hormuz.#21 🎧 @8:32 Tarayyar Turai za ta faɗaɗa matakin kare tattalin arzikin ƙasashen ƙungiyar daga barazanar China.#22 🎧 @8:38 Hukumar Lafiya ta Duniya na tafa da tashin shawo kan cutar Ebola da ke zama barazana ga harkokin kiwon lafiya a Afirka.== DWHausa Rana 2026-05-28 ==Mai gabatarwa: Khadija Ahmad Rufa’i#23 🎧 @9:10 A Gabas ta Tsakiya, yayin da Iran ke kai hare-haren ramuwar gayya ga Amurka, Shugaba Trump na barazanar faɗaɗa hare-harensa kan Oman.#24 🎧 @9:20 Tarayyar Najeriya na kashe tirilolin naira a ɓangaren hanyoyin sadarwa.#25 🎧 @9:28 A Jamhuriyar Nijar, ana sa ran tsaro zai inganta bayan wasu matasa ‘yan daba sun amince da ajiye makamansu.#26 🎧 @9:51 Ɗalibai da dama sun mutu sakamakon tashin gobara a wata makarantar kwana ta ƙasar Kenya.#27 🎧 @9:56 Jagoran addinin Iran ya zargi Amurka da Isra’ila da neman durƙusar da ƙasarsa.#28 🎧 @10:03 Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi hasashen cewa yanayin zafi zai kai ƙololo tsakanin shekaru biyar masu zuwa.== DWHausa Yamma 2026-05-28 ==Mai gabatarwa: Khadija Ahmad Rufa’i#29 🎧 @10:30 A jihar Kano, yayin da ake ci gaba da dambarwar siyasa kan ɗan takarar gwamnan jihar a jam’iyyar ADC, ana kuma ci gaba da dambarwa kan masarautar jihar bayan hawan Sallah na sarakuna biyu.#30 🎧 @10:45 A Jamhuriyar Nijar, ƙungiyoyin direbobin kabu-kabu da masu adaidaita sahu sun yi yunƙurin taimakawa wajen yaƙi da matsalar shan miyagun ƙwayoyi.#31 🎧 @10:54 Habasha ta ɗauki matakin murƙushe ‘yan adawa saboda fargabar ɓarkewar rikici gabanin zaɓen majalisar dokokin ƙasar.#32 🎧 @11:23 Ƙasashen Amurka da Iran sun zargi juna da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da ke tsakaninsu.#33 🎧 @11:29 Tsohon shugaban ƙasar Yemen, Abd Rabbu Mansur Hadi, ya rasu a ƙasar Saudiyya.#34 🎧 @11:34 Kotun tsarin mulkin Madagascar ta yi watsi da buƙatar tsige sabon shugaban mulkin sojan ƙasar.== RFIHausa Safe 2026-05-28 ==Mai gabatarwa: Shamsiyya Haruna#35 🎧 @12:08 Yayin da Amurka ta sake kai sabon hari kan sansanonin sojin Iran, rundunar juyin juya halin ƙasar ta fara mayar da martani tare da gargaɗi cikin kakkausar murya.#36 🎧 @12:21 Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar ya zama halastaccen ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar ADC.#37 🎧 @12:26 Uganda ta rufe iyakarta da Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo domin kauce wa bazuwar cutar Ebola.== RFIHausa Yamma 2026-05-28 ==Mai gabatarwa: Ummaru Sani#38 🎧 @12:57 Jam’iyyar adawa ta ADC ta tsayar da tsohon mataimakin shugaban Najeriya Atiku Abubakar a matsayin ɗan takararta a zaɓen shugaban ƙasa da ke tafe.#39 🎧 @13:11 Jamhuriyar Nijar ta karɓi ɗaruruwan ‘yan gudun hijirar Najeriya da suka tsere wa hare-haren mayaƙan Lakurawa a wasu sassan jihar Kebbi.#40 🎧 @13:20 Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya umurci dakarun ƙasarsa su ƙwace iko da kusan kashi saba’in na Zirin Gaza duk da yarjejeniyar tsagaita wuta.== CRI / CGTN Hausa 2026-05-28 ==#41 🎧 @13:58 Shugaban ƙasar Sin ya amsa wasiƙar da ɗaliban ƙasashen Sin da Amurka da ke haɗa ƙarsa da zumunta tsakaninsu suka aiko masa.#42 🎧 @14:08 Ƙasar Sin za ta bai wa waken kofi na ƙasashen Afirka hamsin da uku damar shiga kasuwarta tun daga ranar ashirin ga watan Yuli bana.#43 🎧 @14:13 Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Tarayyar Najeriya ya jinjina wa sadaukarwa da juriyar ‘yan Najeriya, wanda hakan a cewarsa ke haifar da sakamako mai kyau. This is a public episode. If you would like to discuss this with other subscribers or get access to bonus episodes, visit hausa.substack.com
NOW PLAYING
Kanun Labaran Hausa na 2026-05-28 (HausaRadio.net Headline news)
No transcript for this episode yet
Similar Episodes
Aug 19, 2025 ·1m
Aug 12, 2025 ·40m
Jul 1, 2025 ·28m
Jun 24, 2025 ·38m