EPISODE · Mar 20, 2026 · 3 MIN
Kanun Labaran Hausa na Jumu'a, Ranar Salla 2026-03-20
from Hausa Newsletter · host Hausa Radio News Headlines
2026-03-20 FridayBBC Hausa SafeFull show | Mai gabatarwa: Imam Saleh* Shugabar ruƙun ƙwarya ta Venezuela Delcy Rodríguez ta sauya manyan kwamandojin sojojin ƙasar kwana guda bayan da ta naɗa sabon ministan tsaro.* Iran na cigaba da yin lugudan wuta cikin dare kan Isra’ila.* Gwamnan jihar Borno a Najeriya Baba Gana Umar Zulum ya shaidawa BBC cewa har yanzu akwai tsawan mahara biyu da ke cikin Maiduguri, babban birnin jihar da niyyar kai harin ƙunar baƙin wake kan jama’a.* Mutane biyar (5) ne suka shiga Maiduguri masu suicide bombers. Uku (3) sun tada shi, biyu (2) ba su tada ba. Muna kan neman su. Muna kan bincike. Yanzun nan yadda nake miki magana, mutane su yi hankali ranar Sallah nan.* Yayin da yau take ƙaramar sallah a Najeriya da ƙasashe da dama na faɗin duniya, ko me yafi muhimmanci ga musulmi a wannan rana?* Na farko shi ne akwai sadaka da ake fitarwa ta fidda kai. Kaga zamu iya cewa ranar sallah rana ce ta jinƙai, ta tausayi, ta rahama, ta taimako, ta ba da abinci ga waɗanda basu da hali.DW Hausa SafeFull show | Host mai gabatarwa: DW Hausa’s Muntaqa Ahiwa.* Ranar Salla* To a cikin shirin, yau take sallah a Najeriya da ma wasu sauran sassa na duniya kuma gabanin fara shagulgulan sallar a nan gaba kaɗan, za mu kawo muku bayanan shehunan malamai kan yadda ya dace musulmi ya more wa wannan rana.* A can kudu maso yammacin Najeriya akwai wato bukukuwar da zamu kawo muku na sallar da ke gudana a can.* Sannan mu je jamhuriyar Nijar mu ji yadda su ma suke ci gaba da shagulgulan bayan hawan idi da akayi a ƙasar a jiya Alhamis.* Isra’ila ta maida martani kan wasu jerin hare-hare da suka fito daga ƙasar Iran.* Gwamnati na shirin maganta yawan tashin farashin makamashi a faɗin ƙasar Jamus sakamakon halin da duniya ta shiga.* Shugaban Amurka ya shirya amincewa da wata alama ta tarihi da za ta kasance ɗauke da hotonsa.RFI HausaLabaran RFI Hausa na ƙarfe 8 na safe agogon Najeriya da Nijar 19-03-2026… • RFI Hausa | Host mai gabatarwa: Nasiru Sani* Iran ta baiwa waɗanda ke zaune a keweyen ma’aikatun man fetur na ƙasashen Saudiya, Qatar da kuma Haɗaɗɗai Daular Laraba (UAE) da su fice daga yankin da su ke.* Sannan rundunar sojan Najeriya ta tabbatar da sahihancin wani faifan bidiyo da ke zagayawa a ƙasar a kan wata nasara da ta samu a kan ƴan ta’addan ƙasar.* Sannan ƙasashen Afirka za su ciro bashin dala biliyan ɗari da hamsin da biyar ($150B) a ƙoƙarinsu na ganin cewa sun bunƙasa harkokin kasuwanci na yankin nasu. This is a public episode. If you would like to discuss this with other subscribers or get access to bonus episodes, visit hausa.substack.com
NOW PLAYING
Kanun Labaran Hausa na Jumu'a, Ranar Salla 2026-03-20
No transcript for this episode yet
Similar Episodes
Aug 19, 2025 ·1m
Aug 12, 2025 ·40m
Jul 1, 2025 ·28m
Jun 24, 2025 ·38m