EPISODE · Apr 19, 2026 · 4 MIN
Kanun Labaran Hausa Radio News Headlines 2026-04-19
from Hausa Newsletter · host Hausa Radio News Headlines
2026-04-19 Sunday LahadiBBC HausaMai gabatarwa: BBC Hausa’s Imam SalehHausaRadio.net/BBC Hausa/Kanun Labaran BBC Hausa Radio News Headlines na 2026-04-19* To a cikin shirin na mu na yanzu za ku ji cewa shugaban majalisar dokokin Iran--Muhammad Baghir Ghalibaf--ya yi gargaɗin ci gaba da taƙaita zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigar Hormuz matsawar Amurka ba ta janye shingen da taiwa jiragen ruwan Iran ba. 🎧* Isra’ila ta ce wani sojin ta ya mutu yayin gumurzu da mayaƙan Hezbollah a kudancin Lebanon jiya Asabar. 🎧* A Najeriya kuwa ana ci gaba da ƙorafi a kan yadda ake zargin sakaci da aiki na cigaba da janyo mutuwar majinyata a asibitin koyarwa na Jami’ar Maiduguri, babban birnin jihar Borno. 🎧* “Zuciyar mara lafiyar in ta tashi allun fashinta ya yanke. Daga ranan ba ta sake yin magana ba. Ta suma ta cika koma har Allah ya mata rasuwa. Gabbaɗayenmu nan sai da feshar namu suka mutu ba wanda ya fita wallahi tallahi.”* Har wa yau a Najeriya ‘yan fansho a jihar Nasarawa na ci gaba da ƙorafi a kan yadda haƙƙoƙinsu suka maƙale a hannun hukumomi sama da shekara biyar bayan kammala aiki. 🎧* “Wasu sun ma mutuwa fian kunda denda ba’a biya ba. Suna ciwo an anje asibiti ba kudi biyan asibiti. Shekara talatin da biyar mun ritaya amma ba a komi inda zamu shiga shi abun da gwamnati ta bamu.”2026-04-18 Saturday AsabarDW HausaHausaRadio.net/DW Hausa/2026-04-18 AsabarMai gabatarwa (host): Abdurahman Hassan* A cikin shirin na yanzu, muna tafe da shirye-shirye waɗanda suka haɗa da shirin Ji ka Ƙaru da Zaɓi Sonka, sai kuma Ra’ayin Malamai. 🎧* Iran ta ce ta samu sabon tayin sulhu daga Amurka don tattaunawa da nufin kawo ƙarshen yaƙin da ake yi a Gabas ta Tsakiya. 🎧* Papa Roma Leo na goma sha huɗu ya yada zango a yau a ƙasar Angola bayan ya fito daga ƙasar Kamaru. 🎧* Dubban mutane sun yi zanga-zanga a faɗin Jamus suna kiran da a gaggauta sarra/sauya tsarin makamashi zuwa wanda ake sabuntawa. 🎧RFI HausaHausaRadio.net/RFI Hausa/2026-04-18 AsabarMai gabatarwa (host): RFI’s Azima Bashir Aminu* Shugaba Tinubu na Nigeria ya sanya hannu a kasafin kuɗin ƙasar na naira tiriliyan sittin da takwas. 🎧* Ma’aikata fiye da dubu guda za su rasa guraben ayyukansu a Kenya bayan farraƙa tsakanin kamfanonin Meta da Sama. 🎧* Amurka ta ce tana da sojojin ruwa fiye da dubu goma da za su tabbatar da datse jiragen Iran daga zirga-zirga a teku. 🎧2026-04-17 Friday Juma’aRFI HausaHausaRadio.net/RFI Hausa/2026-04-17 Friday* Masu sauraro, barkanmu da yammaci ga kanun labaran. 🎧* Iran ta buɗe mashigin Hormuz na kwanaki goma tare da baiwa dukkanin jirage damar zirga-zirga. 🎧* A Najeriya, ɓacewar Naira tiriliyan talatin da huɗu (~$25.3B) daga kuɗaɗen shigar ƙasar ya janyo cece-kuce daga ‘yan fafutuka. 🎧* Amnesty International ta yi kakkausar suka ga matakin Burkina Faso na dakatar da ƙungiyoyin fararen hula fiye da ɗari. 🎧 This is a public episode. If you would like to discuss this with other subscribers or get access to bonus episodes, visit hausa.substack.com
NOW PLAYING
Kanun Labaran Hausa Radio News Headlines 2026-04-19
No transcript for this episode yet
Similar Episodes
Aug 19, 2025 ·1m
Aug 12, 2025 ·40m
Jul 1, 2025 ·28m
Jun 24, 2025 ·38m