EPISODE · May 21, 2026 · 14 MIN
Kanun Labaran BBC - DW - RFI - CRI Hausa na 2026-05-21 (HausaRadio.net News Headlines)
from Hausa Newsletter · host Hausa Radio News Headlines
Ƙarin bayani: https://hausadictionary.com/HausaRadio.net/2026-05-21== BBCHausa Safe 2026-05-21 ==Mai gabatarwa: Ibrahim Yusuf Muhammad#1 🎧@0:14 Shugaban Cuba Miguel Díaz-Canel ya yi watsi da tuhumar da Amurka ta yi wa magabacinsa Raúl Castro, yana cewa hakan bita da ƙulli ne na siyasa.#2 🎧@0:28 Wata tawagar ‘yan ci-rani ‘yan asalin Ghana da ke Afirka ta Kudu za ta koma ƙasarta domin tsere wa zanga-zangar ƙin jinin baƙi.#3 🎧@0:33 A Najeriya, taƙaddama ta ƙware tsakanin masu neman takarar shugabancin ƙasa a jam’iyyar ADC, inda tsohon ministan sufuri Rotimi Amaechi ya yi iƙirarin cewa Atiku Abubakar ba zai iya lashe zaɓe ba ko da ya zama ɗan takarar jam’iyyar.#4 🎧@1:04 A Jamhuriyar Nijar, manoma a jihar Diffa sun koka kan mawuyacin halin da suka shiga sakamakon matsalolin da ke kawo cikas ga ƙoƙarin tabbatar da wadatar abinci a ƙasar.#5 🎧@1:34 A ƙasar Mali, masu iƙirarin jihadi sun banka wasu motocin sufuri wuta a kusa da babban birnin ƙasar.== BBCHausa Hantsi 2026-05-21 ==Mai gabatarwa: Ibrahim Yusuf Muhammad#6 🎧@1:58 Maimaicin labarin shugaban Cuba Miguel Díaz-Canel da ya yi watsi da tuhumar Amurka kan Raúl Castro.#7 🎧@2:07 Dangantaka na ci gaba da tsami tsakanin Colombia da Bolivia bayan da ƙasashen biyu suka janye jakadunsu.#8 🎧@2:16 A Najeriya, ma’aikatan asibitin gwamnatin tarayya masu jinyar masu lalurar ƙwaƙwalwa da ke Enugu sun shiga wani yajin aiki na sai abin da hali ya yi.#9 🎧@2:28 A fagen wasanni, masana sun fara tsokaci ko Mikel Arteta zai iya jagorantar Arsenal zuwa ƙarin nasarori bayan lashe gasar Premier ta bana.== BBCHausa Rana 2026-05-20 ==Mai gabatarwa: Umaima Sani Abdulmumin#10 🎧@3:26 Sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio ya yi tayin inganta dangantaka tsakanin Amurka da Cuba.#11 🎧@3:35 Gwamnatin Birtaniya na shan suka kan matakin sassauta wasu takunkuman mai da iskar gas na Rasha.#12 🎧@3:42 A jihar Kano, 'ya'yan wani ɗan sanda da ya rasa ransa a bakin aiki sun roƙi a yi musu adalci.#13 🎧@4:05 Gwamnatin mulkin soja a Nijar ta kafa dokar ƙayyade kuɗin haya da nufin shawo kan tsadar gidaje a faɗin ƙasar.== BBCHausa Yamma 2026-05-20 ==Mai gabatarwa: Umaima Sani Abdulmumin#14 🎧@5:04 Gwamnatin Amurka ta gabatar da tuhumar manyan laifuka kan tsohon shugaban Cuba Raúl Castro.#15 🎧@5:16 Hoton bidiyon da ministan tsaron Isra'ila ya wallafa, wanda ke nuna yadda ake muzgunawa wasu masu fafutukar kai agaji Gaza, ya haifar da cece-kuce.#16 🎧@5:26 A Najeriya, iyaye da malamai sun yi zanga-zanga kan garkuwa da ɗalibai da kisan gillar da aka yi wa wani malamin makaranta a yankin Ogbomosho na jihar Oyo.#17 🎧@5:45 A jihar Kano, hukumar kashe gobara ta yi ƙarin haske kan abin da ya haddasa haɗarin motar da ta faɗa cikin dam ɗin Thomas a ƙaramar hukumar Ɗanbatta.== DWHausa Safe 2026-05-21 ==Mai gabatarwa: Abdulkarim Muhammad Abdulkarim#18 🎧@6:37 Gwamnatocin jihohin Katsina da Zamfara sun musanta zargin wasu masu neman takara a jihohinsu na cewa an murƙushe buƙatunsu.#19 🎧@6:47 Masana shari'a na nazarin batun yiwuwar takarar tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ta fuskar gyaran kundin tsarin mulkin 2018.#20 🎧@6:57 Ƙwararru a fannin hada-hadar tashoshin ruwa sun ja hankalin mahukunta a nahiyar Afirka domin sakan musu mara cikin ayyukansu.#21 🎧@7:12 Ƙungiyar AES ta Nijar, Mali da Burkina Faso ta buɗe dandalin musayar ra'ayoyi da dabarun yaƙi da ta'addanci a Sahel.#22 🎧@7:31 Iran ta aiwatar da hukuncin kisa ga mutane biyu da take zargi da ayyukan ta'addanci da tona asirinta.#23 🎧@7:37 Koriya ta Kudu da Amurka sun tattauna hanyoyin ƙarfafa tsaron iyakokin Koriya ta Kudu.#24 🎧@7:43 'Yan tawaye a gabashin lardin Papua na Indonesia sun kashe kusan masu haƙar ma'adanai goma.== DWHausa Rana 2026-05-20 ==Mai gabatarwa: Abdullah Tanko Bala#25 🎧@8:04 Jam'iyyar adawa ta NDC a Najeriya ta tsayar da Peter Obi a matsayin ɗan takararta na zaɓen shugaban ƙasa mai zuwa.#26 🎧@8:30 A Jamhuriyar Nijar, al'umma na ci gaba da bayar da ra'ayoyinsu kan dokar ƙayyade farashin kuɗin haya da gwamnatin mulkin soja ta yi.#27 🎧@8:59 Kasuwannin hannun jari a Turai da Asiya sun farfaɗo, yayin da Tarayyar Turai ta amince da tallafin Jamus a fannin makamashi mai sabuntawa.#28 🎧@9:11 An gabatar da ayar doka a majalisar dokokin Isra’ila domin kiran sabon zaɓe.== DWHausa Yamma 2026-05-20 ==Mai gabatarwa: Abdullah Tanko Bala#29 🎧@9:41 Fitowar tsohon shugaban Najeriya Goodluck Jonathan domin takarar shugaban ƙasa a 2027 na shirin jefa siyasar Najeriya cikin babban ruɗu, amma jam'iyyar APC ta ce ba ta jin tsoro.#30 🎧@10:13 Ƙasar Kamaru ta gudanar da bikin ranar haɗin kan ƙasa karo na hamsin da huɗu.#31 🎧@10:35 A Jamhuriyar Nijar, ƙungiyar ƙasashen Sahel ta AES ta buɗe dandalin tattaunawa kan 'yan ta'adda da masu ɗauke da makamai da suka amince su miƙa wuya domin zaman lafiya.#32 🎧@11:07 Mahukuntan Iran sun ce suna shirye da duk wani farmaki daga Amurka.#33 🎧@11:12 Sabon Firayim Ministan Hungary ya kai ziyarar aiki ta farko zuwa ƙasar waje.#34 🎧@11:17 Hukumomin agaji na ƙara matsawa wajen daƙile cutar Ebola a yankin tsakiyar Afirka.== RFIHausa Yamma 2026-05-20 ==Mai gabatarwa: Michael Kudison#35 🎧@11:53 Rundunar tsaron Najeriya ta ce akwai manyan kwamandojin 'yan ta'adda da ta kashe a samamen haɗin gwiwa da sojan Amurka.#36 🎧@12:02 Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce za ta yi amfani da rigakafin gwaji yayin da sabon nau'in cutar Ebola ke ci gaba da yaɗuwa da kisa.#37 🎧@12:13 Ƙasashen Rasha da China sun yi gargaɗi kan yadda ake watsi da mutunta dokokin duniya.== RFIHausa Safe 2026-05-21 ==Mai gabatarwa: Shamsiyya Haruna#38 🎧@12:42 Fadar shugaban Najeriya ta jaddada buƙatar a bar mambobin jam'iyyar APC su zaɓi ɗan takarar da suke so, yayin da masana ke ganin Shugaba Tinubu ne uwar matsalar rikicin jam'iyyar.#39 🎧@13:01 Rukuni na farko na baƙin hauren da Amurka ta kora, ciki har da ɗan Najeriya ɗaya, sun sauka a ƙasar Sierra Leone.#40 🎧@13:06 Shugaba Trump ya ba wa Iran wa'adin kwanaki biyu ta amince da sharuɗɗan da aka gabatar mata, ko kuma ta fuskanci mummunan harin soja.== CRI / CGTN Hausa 2026-05-21 ==Mai gabatarwa: Fa’iza Muhammad Mustafa#41 🎧@13:38 Tawagar Jam’iyyar Kwaminista ta ƙasar Sin ta ziyarci ƙasashen Masar da Tanzania.#42 🎧@13:44 WHO ta ce halin cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo da Uganda bai kai matsayin ayyana matakin gaggawa na bazuwar annoba ba.#43 🎧@13:48 Hulɗar Sin da Rasha ba za ta canja ba duk da sauye-sauyen da ake fuskanta a duniya. This is a public episode. If you would like to discuss this with other subscribers or get access to bonus episodes, visit hausa.substack.com
Embed this episode
Ready to play
Kanun Labaran BBC - DW - RFI - CRI Hausa na 2026-05-21 (HausaRadio.net News Headlines)
No transcript for this episode yet
Similar Episodes
No similar episodes found.