PODCAST · news
Mu Zagaya Duniya
by RFI Hausa
Shirin Mu Zagaya Duniya na duba Wasu Muhimman Labarai da suka ja hankalin Duniya a cikin mako. Ana gabatar da shirin ne a ranar Asabar da safe a kuma maimaita ranar Lahadi da daddare.
-
24
Dangote ya buɗewa al'uma ƙofar shiga a dama dasu a harkokin matatar mai
Shirin mu zagaya Duniya na wannan ya ba da hankali ne akan yadda Attajirin Afirka Aliko Dangote ya buɗe ƙofar sayar da hannayen jari ga jama'ar Najeriya, sai kuma matakin da mahukuntan Nijar suka ɗauka na umartar masu ababen hawa dasu je Yamai babban birnin ƙasar domin duba lafiyar ababen hawansu, sai batun ladan da Shigaban Amurka Donald Trump ya sanya ladan Dala dubu biyar-biyar ga Amurkawa idan har jam'iyarsa ta Republican ta samu nasara a zaɓen tsakiyar wa'adi.
-
23
Yunkurin juyin mulki a Nijar ya ci gaba da ɗaukar hankali a faɗin duniya.
A wannan makon shirin Mu Zagaya Duniya ya yi waiwayen kan sukar kalaman shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu da ya yi na cewa arewacin kasar ya fi amfana da manufofinsa, sai batun juyin yunkurin juyin mulkin Nijar da ya dauki hankali, sai rahoton MDD da ya gano katsalandan din kasashen waje ne ke rura wutar rikicin Sudan, sai luguden wutar da aka yi musaya tsakanin Amurka da Iran da ya janyo asarar rayuka. A Najeriya, jam’iyyun adawa sun fara tsara yadda za su kayar da gwamnatin APC mai mulkin ƙasar ta wajen haɗakar da za ta fitar da ɗan takara ɗaya mai ƙarfi da zai iya gwabzawa da shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027, inda ƙungiyar G-100, wadda ta tsara wannan haɗaka ta kawo shawarar cewa duk wanda ya samu takarar, zai yi wa’adi guda na shekaru 4 ne kacal. Haka zalika, ikirarin da shugaba Bola Tinubu ya yi cewa yankin arewacin ƙasar ce ta fi cin gajiyar manufofinsa na sauye-sauyen tattalin arziƙi ya janyo suka daga masu ruwa da tsaki, inda ƙungiyar al’ummar Arewacin ƙasar da wasu ƙungiyoyin yankin suka caccaki kalaman, su na mai cewa a maimakon cigaba, manufofin shugaban sun mayar da yankin arewa cibiyar talauci. A gefe guda kuma, gwamnatin mulkin sojan Nijar zargi Ivory Coast, Benin, Faransa, Chadi da kuma ECOWAS da kitsa shirin kifar da gwamnati, biyo bayan wani bore da ya faru a ranakun 28 zuwa 29 ga watan Agusta, da kuma haifar da rarrabuwar kawuna, musamman a tsakanin rundunar soji. Yayin da ake tsaka da damana har ma aka fara tunkarar alamomin kaka, har yanzu akwai wasu garuruwa 20 na yankin Damagaram da ba su samu saukar ruwan shuka ba a Ƙaramar Hukumar Gangara na gundumar Tanut. Mafi yawanci damina Niger bata wuce wata 3 zuwa 4, domin dai tana ƙarewa a watan Satumba in ta yi tsawon watan Oktoba. Domin jin cikakken shirin, latsa alamar sauti.
-
22
Adadin mutanen da suka mutu a ambaliyar ruwan Nepal na ci gaba da ƙaruwa
Shirin ''Mu Zagaya Duniya" tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako, ya taɓo muhimman batutuwan da suka faru a makon da muke bankwana da shi, inda ya taɓo yadda ƴanbindiga suka yi awun gaba da mutum sama da 600 a wani kauye da ke kan iyakar Najeriya da Benin a can jihar Neja. Adadin mutanen da mumunar ambaliyar ruwa ta kashe a Nepal ya haura zuwa 470. A ɓangaren wasanni kuwa, shirin ya yi waiwaye kan rahoto murabus ɗin shugabancin hukumar kwallon kafa ta Najeriya da kuma yadda aka gudanar da bikin ranar Hausa. Ku latsa lamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Shamsiyya Haruna..........
-
21
Mu zagaya Duniya: Fara yaƙin neman zaɓe da musayar yawu tsakanin Tinubu da Atiku
Shirin ''Mu Zagaya Duniya" tare da Shamsiyya Haruna a wannan mako kamar yadda aka saba ya taɓo muhimman batutuwan da suka faru a makon da muke bankwana da shi a Najeriya da sauran ƙasashen Afrika da ma duniya baki ɗaya. Cikin batutuwan da shirin ya taɓo akwai yakin neman zaben Najeriya, inda aka jiyo tsohon mataimakin shugaban kasar Atiku Abubakar na shan alwashin dawo da tallafin man fetur, da kuma raddin shugaba Tinubu kan wannan furuci, sai cikar shekaru goma sha biyar da kifar da gwamnatin shugaban Libya Muammar Ghaddafi, inda a yankin Gabas ta tsakiya muka tabo labarin Iran da ta sanya ladan makudan kudade ga duk wanda ya kamo mata sojojin Amurka dama sauran muhimman labarai daga sassa daban-daban na duniya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
-
20
Waiwaye game da muhimman labarai da suka faru a wannan makon
A Colombia, wata girgizar ƙasa mai karfin maki 7.4 da ta afkawa ƙasar da ke kudancin Amurka tare da hallaka akalla mutane sama da 100, yayin da wasu da dama suka jikkata,a cikin shirin da ke waiwaye game da muhimman abubuwan da suka faru a makon da mu kayi ban kwana,wato Mu zagaya Duniya za ku ji irin wainar da aka tuya a wasu ƙasashe..............
-
19
Saudiya, Pakistan da Turkiya sun sanar da kulla yarjejeniyar tsaro
Ƙasashen Saudiya,Pakistan da kuma Turkiya sun sanar da kulla yarjejeniyar tsaro a tsakanin su yau juma’a a birnin Djeddah a wani yanayi da ake kara samun tashin hankali a yankin Gabas ta Tsakiya. Yarjejeniyar da aka raɗa wa suna yarjeniyar Makka, ko baya ga harakar tsaro ta kuma tanadi faɗaɗa alakar da ke tsakanin ƙasashen a fanoni daban-daban.
-
18
Mu Zagaya Duniya: Zafin alaƙa tsakanin Najeriya da Afrika ta kudu
Shirin "Mu Zagaya Duniya" tare da Oumarou Sani kamar kowanne mako ya taɓo muhimman labaran da suka faru a sassa daban daban na Najeriya ciki har da zafin alaƙa tsakanin Najeriya da Afrika ta Kudu, kana dambarwar ma'aikatar Bogi a Najeriya sai kuma batun cika shekaru 3 da faro mulkin Soji a Najeriya sannan batun ficewar Chadi daga kotun ICC. Zamu soma shirin daga Najeriya inda batun kirkirar ma’aikatar Bogin nan ta PFIPC karkashin jagorancin Adeniyi Adeyimi Mattew wadda ke habbaka hulda da zuba jari ta sake tayar da kura a kasar . Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin.
-
17
Mu zagaya Duniya: Kotu ta yiwa ƴan ta'adda ɗaurin rai da rai a Najeriya
Shirin Mu zagaya duniya tare da Oumarou Sani ya mayar da hankali kan muhimman labaran da suka faru a makon da muke bankwana da shi. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin wanda ya taɓo dukkanin batutuwa kama da tsaro da tattalin arziƙi, siyasar ƙasashe dama rikice-rikice.
-
16
Ceto ɗalibai da malamansu a Oyo na cikin labarai da suka ja hankali a makon jiya
Shirin 'Mu Zagaya Duniya' na wannan makon tare da Oumar Sani ya yi bitar wasu daga cikin manyan labarai da suka fi ɗaukar hankali a makon da muka yi bankwana da shi ciki har da nasarar kuɓutar da dalibai tare da malamansu 40 a jihar Oyo da ke Najeriya bayan sun shafe kwanaki 50 a hannun wadanda su kayi garkuwa dasu.
-
15
Faɗa ya sake ɓarkewa tsakanin Amurka da Iran bayan rugujewar yarjejeniya
Shirin a wannan makon zai leka Gabas ta Tsakiya inda rikici ya sake barkewa tsakanin Amurka da Iran abin da ya kawo karshen yarjejeniyar fahimtar juna ta watanni uku da suka cimma a tsakaninsu. Bayan nan, shirin zai taɓo wasu mahimman lammuran da suka wakana a sassan yammacin nahiyar Afirka, musamman Najeriya, Nijar da Kamaru.
We're indexing this podcast's transcripts for the first time — this can take a minute or two. We'll show results as soon as they're ready.
No matches for "" in this podcast's transcripts.
TOPICS IN THIS SHOW
Loading reviews...
Loading similar podcasts...