PODCAST · news
Bakonmu a Yau
by RFI Hausa
A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.
-
22
Souleyman Yahaya kan tasirin al'ummar Hausawa a ƙasar Togo
Hausawa a ƙasar Togo kamar dai a sauran ƙasashe, sun gudanar da bukukuwan ranar Hausa ta duniya, inda suka yi amfani da wannan damar don tattauna al’adu da kuma tasirin wannan al’umma a cikin wannan ƙasar da ke Yamancin Afirka. Abdoulaye Issa ya zanta da Souleyman Yahaya, shugaban cibiyar yaɗa al’adu da kuma kare muradun Hausawa a Togo, wanda ya yi masa ƙarin bayani a game da yanayin zamantakewarsu a ƙasar. Ga kuma tattaunawarsu. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...
-
21
Alhaji Ibrahim Muhammad kan yadda shirin samar da ɗan takarar adawa ɗaya a Najeriya ya rushe
Hukumar Zaɓen Najeriya ta fitar da jerin sunayen mutane 18 da suka cancanci tsayawa takarar shugabancin ƙasar da mataimakansu, sai kuma wasu mutane dubu 4 da 860 da za su tsaya takarar neman kujerun Majalisun Tarayya a zaɓen da za a yi shekara mai zuwa. Wannan dai na nuni da cewa yunƙurin ƴan adawa na fitar da ɗantakarar ɗaya tilo don tunkarar jam’iyyar mai mulki ya ci tura. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Alhaji Ibrahim Muhammad, shugaban jam’iyyar AMP ɓangaren adawa reshen jihar Kebbi, domin jin matsayinsu dangane da haka.
-
20
An naɗa sabon kwamandan da zai jagoranci yaƙi da ƙungiyoyin ta’addanci a Najeriya
A Najeriya an naɗa sabon kwamandan da zai jagoranci yaƙin da ake da ƙungiyoyin ta’addancin na ISWAP da Boko Haram a arewa maso gabashin ƙasar, lamarin da ke nuni da cewa an maye gurbin wanda ke jagorantar wannan runduna ƙasa da shekaru biyu bayan naɗa shi kenan. Shin wanan sauyi ya dace da halin da ake ciki na yaƙi da ta’addanci ko kuma dai kawai garambawul ne da aka saba yi? Akan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da Detective Awwal Bala Durumin Iya masanin tsaro ne a Najeriya. Shiga alamar sauti domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
-
19
Kamilu Sani Fagge kan tsanantar rikici a Gabas ta tsakiya
Rikicin Gabas ta Tsakiya da ya tsananta tsakanin Amurka da Iran na cigaba da faɗaɗa, inda a ‘yan kwanakin nan ya kai ga sake tayar da rikicin Yemen tsakanin gwamnatin ƙasar da Saudiya ke marawa baya, da kuma ‘Yan tawayen Houthi masu samun goyon bayan Iran, ɓangarorin da zuwa yanzu suka rasa mayaƙa fiye da 500. Baya ga datse mashigin ruwan Hormuz, a halin yanzu rikicin na Gabas ta Tsakiya ya shafi mashigin ruwan Bab al-Mandeb da ke tekun Maliya, inda mayaƙan Houthi ke kai wa manyan jiragen ruwa farmaki don goyon bayan Iran. Don jin yadda masana ke kallon lamarin da kuma haɗarin da ke tattare da shi, Nura Ado Suleima ya tattauna da Farfesa Kamliu Sani Fagge na jami’ar Bayero da ke Kano.
-
18
Hon Sama’ila Mohammed kan saida hannun jarin matatar man Dangote
A ranar Litinin da ta gabata, matatar man fetur ta Ɗangote ta dasa ɗambar shirinta na shiga kasuwar hada-hadar hannayen jari, waɗanda shugaban rukunin kamfanonin na Ɗangote, Alhaji Aliko, ya ce ana iya mallakar aƙalla guda 10 da ƙasa da Naira dubu 6. Kan wannan Nura Ado Suleiman ya tattauna da Honorable Sama’ila Mohammed, masanin tattalin arziƙi a Najeriya, wanda ya yi tsokaci kan tasiri da kuma yadda ‘yan Najeriya musamman masu ƙaramin ƙarfi za su amfana sayen hannayen jarin matatar man ta Ɗangote. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawarsu..............
-
17
Tattaunawa da Datective Auwal Bala kan baiwa MOPOL damar yaƙi da ta'addanci
Rundunar ƴan sandan Najeriya ta sanar da tsaurara matakan yaƙi da ta’addanci da ya addabi ƙasar ta hanyar shigar da ƴan sandan kwantar da tarzoma cikin aikin fatattakar ƴan ta’adda. Da yake jawabi yayin wani rangadi da ya kai barikokin ƴan sanda a jihar Lagos, babban sufeton ƴan sandan ƙasar Tunji Disu ya ce, daga yanzu za’a sanya jami’an cikin aikin gadan-gadan. Game da wannan batu Rukayya Abba Kabara ta tattauna Datective Auwal Bala masanin tsaro a Najeriya. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.
-
16
Dr Salissou Ibrahim Yahaya kan amincewa da yi wa taswirar duniya gyara
Majalisar Ɗinkin Ɗuniya ta amince da ƙudirin da ke bayar da damar yi wa taswirar duniya gyara, bayan da ƙasashen Afirka suka gabatar da ƙorafin cewa wadda ake amfani da ita a yau na ɗauke da kura-kurai tare da tauye faɗin nahiyar na haƙiƙan. Abdoulkarim Ibrahim Shikal ya zanta da Dr Salissou Ibrahim Yahaya, malami kuma masani kimiyar taswirar duniya a Jami’ar Damagaram da ke Jamhuriyaer Nijar, wanda ya yi muna ƙarin bayani a game da wannan taƙaddama da aka jima ana yi. Ku latsa alamar sauti don sauraron zantawarsu................
-
15
Martani kan iƙirarin shugaban Najeriya game da ciyar da arewacin ƙasar gaba fiye da kowanne yanki
A Najeriya iƙirarin da shugaba Bola Tinubu ya yi cewa yankin arewacin ƙasar ce ta fi cin gajiyar manufofinsa na sauye-sauyen tattalin arziƙi ya janyo suka daga masu ruwa da tsaki, inda ƙungiyar al’ummar Arewacin ƙasar da wasu ƙungiyoyin yankin suka caccaki kalaman, su na mai cewa a maimakon cigaba, manufofin shugaban sun mayar da yankin arewa cibiyar talauci. Akan haka ne Michael Kuduson ya tattauna da shugaban ƙungiyar tuntuɓa da haɗin kai ta Arewa, Dakta Harris Haroon Jibril, wanda ya fara bayani kamar haka. Danna alamar saurare domin jin cikakkiyar tattaunawar.
-
14
Dr Ibrahim Modibbo kan tattaunawar samar da ɗan takara ɗaya da zai kara da Tinubu
Wakilan Jam’iyyun adawa a Najeriya sun gana a jiya Litinin, inda suka tattauna kan yiwuwar ƙulla yarjejeniyar haɗa ƙarfi wajen mara wa ɗan takara guda baya a zaɓen shugabancin ƙasar da ke tafe a 2027. Wannan taro ya gudana ne a ƙarƙashin jagorancin G-100, ƙungiyar wasu fitattun ƴan Najeriya da ke ƙoƙarin haɗa gamayyar jam’iyyun adawa. Don jin ƙarin bayani kan abinda aka cimma, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Dakta Ibrahim Modibbo ɗaya daga cikin shugabannin ƙungiyar ta G-100. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar tattaunawarsu...........
-
13
Dr Kabiru Adamu kan boren sojoji a Jamhuriyar Nijar
Ƙura ta lafa a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar bayan da wasu sojoji suka kai hari filin jirgin sama da fadar shugaban ƙasar, a wani bore da suka fara tun cikin daren Juma’a zuwa wayewar safiyar Asabar, lamarin da ya haifar da musayar wuta da fashe-fashe na tsawon sa'o'i. Rahotanni na cewa dakarun hayar Rasha sun taimaka wajen daƙile boren na ƙananan sojoji da suka kaucewa fagen daga domin farmakan babban birnin. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar Ahmad Abba da Dr. Kabiru Adamu, masanin tsaro a yankin Sahel.......
-
12
Muhd Makiga kan maƙudan kuɗin fansar da ƴan ta'adda ke samu a Najeriya
A Najeriya masana da wasu ƴan ƙasar na ci gaba da ɗiga ayar tambaya kan rahoton cibiyar binciken tsaro ta SBM Intelligence, da ya nuna cewar ƴan ta’adda sun karɓi kuɗaɗen fansar da yawansu ya kai Dala miliyan 5.8, daidai da kusan naira biliyan 8 cikin shekara guda. Rahoton, ya ce ƴan ta’addan sun ƙarbi kuɗaɗen ne a tsakanin watan Yulin shekarar bara ta 2025, da kuma Yunin bana, kuma mayaƙan Boko Haram ne suka amshe kaso 90 cikin 100 na jimillar kuɗaɗen. Don jin yadda masana tsaro ke kallon wannan batu, Nura Ado Suleiman ya tattauna da Muhd Sani Ibrahim Makiga. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...
-
11
Isa Sunusi kan yadda ƴan siyasa suka fara kalaman tinzira al'umma
Yayin da aka kada gangar siyasar Najeriya, ana zargin wasu ƴan siyasar da kalaman tinzira tashin hankali, abinda ke barazana ga zaman lafiyar jama'a. Bayan Sanatan jihar Osun da ya buƙaci a kashe magoya bayan jam'iyyar adawa, an jiyo shugaban karamar hukumar Kuje dake Abuja na kira ga wadanda basa goyan bayan APC da su fice daga yankin. Tuni wannan ya fara jefa fargaba a tsakanin jama'a. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Daraktan ƙungiyar Amnesty a Najeriya, Malam Isa Sanusi kan lamarin. Latsa alamar sauti don sauraren tattaunawarsu...
-
10
Farfesa Yakubu Magaji Azare kan ranar Hausa ta duniya
Yau ake bikin shekara-shekara na ranar Hausa ta Duniya da aka saba gudanarwa a duk ranar 26 ga Agusta, tun bayan assasa shi a 2015, domin tunatar da muhimmancin Harshe da kuma Al’adun Hausawa. Daga cikin batutuwan da bikin bana zai mayar da hankali kai, akwai amfani da kimiyya da fasaha wajen bunƙasa Harshen Hausa da bai wa Harshen da Al’adun Hausawa kariya daga sauye-sauyen zamani daga kutsen sabbin Al’adu. Ku latsa alamar sauti don sauraran tattaunawar Nura Ado Suleiman da Farfesa Yakubu Magaji Azare, na Jami’ar Bayero da ke Kano a Najeriya............
-
9
MalamShekarau kan yadda jam'iyyar APC ke shirin yin ganganci makamancin na PDP
Masana siyasar Najeriya na gargadin Jam'iyyar APC da ta ɗauki darasi daga PDP wadda bayan ta kwashe shekaru 16 a karagar mulki ƴan ƙasar suka juya mata baya, a daidai lokacin da take cewa sai ta shekara 60 a karaga. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da tsohon gwamnan Kano Malam Ibrahim Shekarau, wanda yanzu haka ɗan takarar Sanata ne a jam'iyyar a zaɓen shekarar 2027 game da kalaman wasu ministocin APC cewar rantsuwa kawai suke jira a shekara mai zuwa, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai.
-
8
Shugaban gwamnonin Tafkin Chadi ya ziyarci N'djamena kan tsaron yankin
Shugaban gwamnonin jihohin dake kewaye da Tafkin Chadi, Gwamnan Jihar Yobe Mai Mala Buni ya ziyarci Ndjamena domin ganawa da jami'an tsaro da kuma yan gudun hijirar da suka makale a can, wanda shi ne irin sa na farko. Bayan kammala ziyarar, ga abinda ya shaidawa Bilyamimnu Yusuf dangane da ziyarar...
-
7
Tattaunawa da Abdullahi Idris kan shirin fara yaƙin neman zaɓen 2027 a Najeriya
A wannan Laraba 19 ga watan Agusta ake ƙaddamar da yaƙin neman zaɓen Najeriya a hukumance, gabanin zaɓen shekara mai zuwa. Ƙwana ɗaya gabani ƴan takarar neman shugancin ƙasa sun rattaba hannu kan yarjejeniyar gudanar da zaɓe cikin kwanciyar hankali ba tare da haifar da rikici ba. Wasu daga cikin yan takaran sun halarci taron, yayin da wasu kuma suka samu wakilci. Dangane da tasirin wannan mataki da kuma tsaftace yaƙin neman zaben, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr Abdullahi Idris, shugaban kungiyar zaman lafiyar Arewa cin Najeriya, kuma idan kuka latsa alamar sauti za ku ji cikakkiyar hirar su...
-
6
Ana ci gaba da tattaunawa kan yarjejeniyar tsaro tsakanin Amurka da Najeriya
Yanzu haka Najeriya da Amurka na ci gaba da tattaunawa da kuma aiwatar da yarjejeniyar tsaron da suka amince da ita a tsakaninsu. Ko a makon jiya, mashawarcin shugaban ƙasar kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya jagoranci tawagar ministoci domin gudanar da irin wannan tattaunawar. Sai dai wasu 'yan Najeeriya na ci gaba da neman ƙarin bayani kan abin da yarjejeniyar ƙasashen biyu ta ƙunsa. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da shugaban kamfanin Beacon, Dakta Kabir Adamu, loacin da ya ziyarci RFI Hausa. Shiga alamar sauti, domin sauraron cikakkiyar tattaunawar.
-
5
Tattaunawa kan darusan aka koya daga zaɓen gwamnan Osun
A Najeriya, Gwamnan mai ci kuma ɗan takarar jam’iyyar Accord Ademola Adeleke ya lashe zaɓen jihar Osun da aka gudanar ranar Asabar da sama da kuri’u dubu 511, yayin da abokin karawarsa na APC mai mulkin ƙasar Bola Oyebamiji ya zo na biyu da banbancin kuri’u 66,252. Kafin ranar zaɓen dai an fuskanci dambarwar siyasa da rikece-rikece da suka yi sanadin mutuwar kusan mutum 40. Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar da Ahmad Abba ya yi da Farfasa Kamilu Sani Fage, masanin siyasa kan zaɓen..
-
4
Muna iyaka ƙoƙarinmu wajen ganin an yi zaɓen Osun ba tare da matsala ba - INEC
A ranar Asabar 15 ga watan Agustan 2026 ake sa ran gudanar da zaɓen gwamnan jihar Osun, wanda tuni ya yi sanadin halaka mutane sama da 30 a lokacin yaƙin neman zaɓe. Rundunar 'Yansanda dai ta tura muƙaddashin Sifeto Janar Isyaku Muhammmad da Kwamishinoni 30 da kuma wasu ƙarin jami'ai dubu 15,000, domin tabbatar da tsaron masu kaɗa ƙuri'u da jami'an zaɓen. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Hajiya Zainab Aminu Abubakar, mai magana da yawun hukumar zaɓen ta Najeriya.
-
3
Farfesa Muhammad Dukku kan gazawar jihohi wajen karɓar tallafin inganta Makarantu
Hukumar kula da ilimin Firamare a Najeriya ta roƙi gwamnonin ƙasar da su yiwa Alla su je su karɓi naira biliyan 332 waɗanda yanzu haka ke ajje a Banki, domin inganta ilimi a jihohinsu. Shugabar hukumar Aisha Garba ta ce baya ga naira biliyan 65 da aka ware domin kai ɗaukin gaggawa, akwai kuma naira biliyan 267 da ke ajje domin amfanin jihohin. Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Farfesa Muhammad Dukku, tsohon shugaban hukumar kula da ilimin Firamare a jihar Gombe ga kuma tattaunawarsu. Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar.......
-
2
Ƴunkuri na hadin kai na ƴan adawa domin fidda dan takara guda a Najeriya
Yan adawar Najeriya sun fara wani sabon yunkuri na hadin kai a tsakanin su domin fidda dan takara guda da zai fafata da shugaban kasa Bola Tinubu a zaben shekara mai zuwa. Wata kungiyar dake kiran kan ta G100 ke jagorancin wannan sabon yunkuri, yayin da ta sanar da taron da za ta yi a makon gobe. Dr Ibrahim Modibbo na daya daga cikin shugabannin ta, kuma ya yi wa Bashir Ibrahim Idris a tattaunawar da suka yi kan lamarin
-
1
Koma bayan da ƙungiyoyin kwallon ƙafar Najeriya ke fuskanta a harakar wasanni
Ga alama ƴan Najeriya da dama sun fusata da yadda ƙungiyoyin kwallon ƙafa na ƙasa ke cigaba da samun nasara a wasannin da suke a nahiyar Afirka. Bayana gazawar da ƙungiyar Super Eagles ta yi na kasa zuwa gasar cin kofin duniya da aka kammala a Amurka da Canada da kuma Mexico, yanzu kuma Super Falcons ta mata ta gaza samun nasara a gasar WAFCON Shiga alamar sauti don sauraron cikakkiyar hirar da Bashir Ibrahim Idris ya yi da Alhaji Yusuf Musa Sakatare a ma'aikatar wasanni ta jihar Nasarawa.....
-
0
Dalilan da suka sa ƙasashe ke rububin ƙulla alaƙa da Ɗangote
Fitaccen attajirin Najeriya Aliko Ɗangote yau ya zama fuskar Afrika a harkokin kasuwanci, da zuba hannayen jari, inda shugabannin ƙasashen Duniya ke nemansa ruwa a jallo domin zuba jari a ƙasashensu ta hanyar samar da masana'antu. Bayan samar da gagarumar matatar man fetur a Najeriya, a kan dala biliyan 20, wadda a yau kimarta ya zarce Dala biliyan 40, yanzu haka ya fara aikin faɗaɗa ta domin zama mafi girma a Duniya, baya ga shirinsa na gina wata sabuwar matatar man a Gabashin Afrika. Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da masanin tattalin arziƙi, Hon Sama'ila Muhammad, a kan wannan shahara ta Ɗangote. Sai a latsa alamar sauti da ke sama domin sauraron wannan tattaunawa.
-
-1
Umar Kwairanga kan yadda kasuwar hannayen jarin Najeriya ta yi zarra a duniya
Masu ruwa da tsaƙi a harkokin tattalin arziki sun yabawa Najeriya dangane da ci gaba da kasuwar hannayen jarin ƙasar da ta zama ta farko a duniya, wajen zarce ta Seoul da London da kuma New York, sakamakon wasu sauye sauye da aka aiwatar. Domin sanin irin matakan da suka samar da wannan ci gaba, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dr. Umar Kwairanga shugaban majalisar gudanarwar hukumar kula da hada-hadar hannayen jarin Najeriya, lokacin wata ziyara da ya kawo ofishin RFI Hausa a Lagos.
-
-2
Tattaunawa da Dr Dauda Kontagora kan koma baya a shirin samar da kuɗin ECO
Shirin samar da kudin bai ɗaya na ƙasashen ECOWAS ya sake samun koma baya saboda sanarwar ƙasar Guinea na ficewa. Domin sanin tasirin matakin da kuma abinda ke iya haifarwa, Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Dakta Dauda Muhammad Kontagora, masanin tattalin arziki a Najeriya, kuma ga yadda zantawar su ta gudana a kai. Ku latsa alamar sauti don sauraron tattaunawar.
We're indexing this podcast's transcripts for the first time — this can take a minute or two. We'll show results as soon as they're ready.
No matches for "" in this podcast's transcripts.
No topics indexed yet for this podcast.
Loading reviews...
ABOUT THIS SHOW
A kullum mukan gayyaci masana a fannoni daban daban domin tattauna wasu muhimman al'amurra da suka shafi kanun labarai a duniya. wani lokacin kuma wasu manyan jami'an gwamnati da masu fada aji sukan kawo muna ziyara domin tattauna batutuwan da suka shafi matsalolin da suka shafe su ko kuma ci gaban kasa.
HOSTED BY
RFI Hausa
Loading similar podcasts...