PODCAST · news
Najeriya a Yau
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
-
958
Me Ya Sa Mutane Suka Dawo Daga Rakiyar Kirifto?
Send us Fan MailA ’yan watanni da suka gabata, matasa da yawa a Najeriya sun dukufa don ganin hakar su ta cimma ruwa wajen samun kudaden kirifto.Amma alamu na cewa a baya-bayan nan wasu daga cikinsu sun sare sun kuma saduda sun dawo daga rakiyar harkar.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan dalilan wasu matasan na yin watsi da harkar kirifto.
-
957
Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari
Send us Fan MailDuk da cewa gwamnati na da dubban kwararrun malamai a makarantunta, har yanzu ana ganin ɗaliban makarantun gwamnati na kasa da na makarantun masu zaman kansu wajen ƙoƙari da kuma sakamakon jarabawa. Wannan matsala ta daɗe tana jawo muhawara tsakanin iyaye, malamai da hukumomin ilimi.Wasu na ganin matsaloli ne da ba za su rasa nasaba da rashin kulawa da watsi da harkar ilimi da gwamnati ta yi ba.Ko wadanne dalilai ne suka daliban makarantun masu zaman kansu suka fi kokari idan aka kwatanta da daliban makarantu na gwamnati?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
-
956
Masu Nau'in Jinin AS Sun Fi Masu Nau'in AA Lafiya
Send us Fan MailSau da dama wadanda ke dauke da nau’in jini na AA na bayyana cewa sun fi kowa lafiya.Suna bayyana cewa basa rashin lafiya kamar yadda masu sauran na’ukan jini ke yi.Shirin Najeriya A Yau na wanna lokaci zai yi nazari ne kan ko da gaske ne masu nau’in jini na AA sun fi sauran masu nau’ukan jini lafiya.
-
955
Yadda Masu Yi Wa Kasa Hidima Za Su Ci Arzikin Yankunan Da Suke AIki
Send us Fan MailBayan hadin kai da karfafa fahimtar juna wadanda hidimar kasa take kawowa, akan samu wasu masu hidimar da sukan yi amfani da duk wata dama da suka samu don neman na sakawa a bakin salati.Yayin da wasu masu hidimar kasa sukan kama sana’a ko su saka hannun jari a inda aka tura su, wasu kuwa komawa garuruwansu suke yi bayan sun kammala.Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan irin damar da masu yi wa kasa hidima suke da ita a garuruwan da aka tura su.
-
954
Nasarori Da Kalubalen Da Bankin Musulunci ke Fuskanta A Najeriya
Send us Fan MailA Jamhuriya ta Hudu a Najeriya, wadda ta fara a shekarar 1999, an samu sauye-sauye masu yawa a bangaren tattalin arziki da harkokin kuɗi, ciki har da tasowar bankunan Musulunci. Wannan tsari na banki ya samo asali ne daga buƙatar samar da hanyoyin mu’amala da kuɗi da suka dace da koyarwar addinin Musulunci, wato hanyoyin da ba su ƙunshi riba, da zamba, ko rashin tabbas ba. A farkon lokaci, ra’ayin kafa bankunan Musulunci ya fuskanci muhawara da adawa daga wasu ɓangarori na al’umma, musamman saboda fahimtar da ake yi cewa tsarin na da alaƙa da addini. Sai dai daga bisani, gwamnati da hukumomin kula da harkokin banki, musamman Babban Bankin Najeriya (CBN), sun samar da dokoki da ka’idoji da suka bai wa bankunan Musulunci damar aiki a matsayin bankunan da basa cin riba. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne akan tasowar bankunan musulunci da kalubalen da suke fuskanta.
-
953
Shin Da Gaske Irin GMO Na Da Matsala Ga Amfanin Noma A Najeriya?
Send us Fan MailAlamu na nuna cewa galibin manoma a Najeriya suna da shakku a kan amfani da irin da aka sauya ƙwayoyin halittarsa.Hakan dai na faruwa ne duk da bayanan da wasu masana suka yi game da alfanun wannan iri wanda ake kira GMO ko Genetically Modified Organism a turance.Tuni dai wasu masanan, waɗanda suka shirya wani taron bita ga manema labarai, suka yi gargaɗi game da illolin irin.Ko mece ce gaskiya game da amfani da wannan iri na GMO?
-
952
Dalilan Yaduwar Cutuka A Irin Wannan Lokaci
Send us Fan MailDa zarar damuna ta fara bankawana, yanayi na sanyi da zafi kan fara sallama, wanda hakan kan zo da rashin lafiya dake yaduwa a cikin alumma.Ko wadanne dalilai ne suka sa ake samun yaduwar rashin lafiya a wannan lokaci?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
-
951
Abin Da Dokar Kasa Ta Ce Kan Takarar Tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan
Send us Fan MailBatun siyasar Najeriya ya sake ɗaukar hankali yayin da jam’iyyar PDP ta bayyana cewa tsohon shugaban ƙasa, Goodluck Ebele Jonathan, zai tsaya mata takarar shugaban ƙasa a 2027. Wannan batu ya tayar da muhawara mai zafi a tsakanin masana, da ‘yan siyasa da ma al’umma.Idan za a iya tunawa dai, an rantsar da tsohon shugaban ƙasan, har sau biyu: a karo na farko a shekarar 2010 bayan rasuwar tsohon shugaban kasa Umaru Musa Yar’adua, sannan kuma a karo na biyu a 2011 bayan lashe zaben da ya biyo baya.Amma abun tambayar a nan shine, shin ko me dokar kasa ta bayyana kan takarar tsohon shugaban kasan bayan rantsar dashi har sau biyu kan karagar mulki?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
-
950
Halin Kunci Da Matan Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ke Tsintar Kansu A Ciki
Send us Fan MailSo da yawa matan da aka yi garkuwa dasu kan shiga halin kunci ko da bayan sun kubuta. Yayin da kadan daga cikinsu ke komawa gudanar da rayuwarsu yadda ta kamata, wasu da dama kan tsinci kansu cikin halin damuwa da tagayyara.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokacin ya yi duba ne kan wannan batu da irin shawarwarin da za a basu don fita daga irin wannan kangi.
-
949
Yadda Wasu Al'ummomi Suke Kare Kansu Daga Ambaliyar Ruwa
Send us Fan MailAmbaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya. Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11. Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu. A kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.
-
948
Yadda Talauci Ke Hana Shayar Da Yara Nonon Uwa Zalla A Najeriya
Send us Fan MailGa alama kwalliya ba ta biyan kudin sabulu a fafautukar da ake yi ta ganin iyaye mata sun shayar da jariransu nono Zalla a wata shida na farko. Rahotanni sun ce duk da dadewar da aka yi ana wayar da kai har yanzu matan da suke shayar da yara nono uwa Zalla ba su haura kashi 29 cikin dari ba. Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan dalilan da suke hana mata shayar da ‘ya’yan su nono zalla na watanni shida.
-
947
''Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na''
Send us Fan MailCutar amosanin jini wacce aka fi sani da cutar sikila na cigaba da barazana ga rayukan masu dauke da ita. Wannan cuta na saka masu ita da ‘yan uwan su cikin halin ha’ula’i, a wasu lokutan ma tana haifar da rasa rayukan wasu dake dauke da ita. Rahotannin Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) sun nuna cewa, kusan yara 300,000 ne ake haifa da cutar Sikila a duk shekara a fadin duniya, inda yankin Kudu da Sahara a Afirka ke dauke da kashi 75% na wannan yawan. A Najeriya kadai, ana kiyasta cewa fiye da yara 150,000 ake haifa da cutar Sikila a kowace shekara — hakan ya sa Najeriya ke da mafi yawan masu fama da cutar Sikila a duniya. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan cutar amosanin jini don gano yadda masu fama da ita ke ji a rayuwar su.
-
946
Yadda Raguwar Maniyyatan Najeriya Ke Tasiri Ga Aikin Hajji
Send us Fan MailA kwanakin nan ana samun raguwar kujerun maniyyata aikin Hajji daga Najeriya, abin da ya jawo fargaba ga masu shirin zuwa kasa mai tsarki da kuma masu hidimar su. A da, Najeriya na samun kujeru sama da dubu casa’in daga gwamnatin Saudiyya, amma cikin shekaru kadan da suka gabata adadin ya ragu zuwa kusan dubu sittin da biyar. Ko yaya kara raguwar kujerun maniyyatan Najeriya ke kara tasiri ga Najeriya?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokacin zai yi duba a kai.
-
945
Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su
Send us Fan MailNajeriya tana cikin ƙasashen da suka fi yawan yara a duniya, a cewar Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF). Sai dai a cewar Hukumar ta UNICEF, kusan rabin wadannan yara suna fuskantar kalubale, kama daga cin zarafi zuwa rashin samun kulawa da dai sauran su. Wadannan matsaloli da yara suke fuskanta dai sun dade suna ci wa masu ruwa da tsaki tuwo a kwarya. Yayin da ake bikin Ranar Yara, shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kan halin da ya yara suke ciki a yau.
-
944
Yawan Kudaden Da Ake Bukata Wajen Samar Da 'Yan Sandan Jihohi
Send us Fan MailBatun samar da ‘yansandan jihohi na ƙara ɗaukar hankalin ‘yan Najeriya, musamman a dai-dai lokacin da matsalar tsaro ke ƙara ta’azzara a sassa daban-daban na ƙasar nan. Sai dai, samar da ‘yansandan jihohi ba abu ne mai sauƙi Kamar yadda wasu ke tunani ba. Gwamnatocin jihohi na buƙatar abubuwa masu yawa kafin su iya ɗaukar wannan nauyi, banda batun samar da dokar samar da wadannan ‘yansanda, akwai batun samar da kayan aiki da horo da sauran abubuwa da ake bukata don gudanar da dawainiyar ‘yansandan. Babban abun da jihohi ke bukata don samar da ‘yansanda shine kudaden gudanarwa don samar da wadannan abubuwa da na ambata. Ko nawa kowacce jiha ke bukata don samar da ‘yansanda? Ta wadannan hanyoyi za a bi don samar da wadannan kudade? Wadannan da ma wasu amsoshin shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba akai.
-
943
‘Halin Kunci Ya Sa Muke Zama A Baca A Abuja’
Send us Fan MailHalin matsin tattalin arziki ya tilasta da yawa daga cikin mutane zama a bacoci a garin Abuja da wasu biranen Najeriya. Mutane a birane kamar Abuja da Legas Da Fatakwal na cikin halin matsi sakamakon rashin ingattaccen muhalli.Ko wannen irin rayuwa irin wadannan mutanen ke yi? Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai a yau da ake bikin ranar muhalli ta duniya.
-
942
Yadda Ake Juya Ababen Hawa Zuwa Masu Amfani Da CNG
Send us Fan MailGalibin ’yan Najeriya ba su san amfanin da sauya ababen hawansu daga masu amfani da man fetur zuwa masu amfani da iskar gas ta CNG ke da shi ba, musamman a wannan lokaci da ake fama da tsadar man fetur. ’Yan Najeriya da dama dai suna amfani da man fetur ne saboda karancin wuraren sauya ababen hawan da sauran dalilai. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kan irin abubuwan da ya kamata ’yan Najeriya, musamman masu ababen hawa, su sani game da iskar gas din ta CNG.
-
941
Abun Da Ya Sa Matan Arewa Ke Gujewa Karantar Ilimin Kimiyya
Send us Fan MailMata a Arewacin Najeriya na fuskantar kalubale da dama a fannin karantar kimiyya. Akwai darussan da a mafi yawan lokuta ba mata kadai ba, har da mazan na kaurace musu. Shirin Najeriya a Yau ya yi nazari ne kan dalilan da suka sa matan Arewacin Najeriya ke tsoron karantar ilimin kimiyya.
-
940
Ko Wa'adi Daya Ya Isa Wanda Aka Zaba Cika Alkawuran Da Ya Dauka?
Send us Fan MailDuk bayan shekaru hudu, Najeriya na kara yin zabe kuma ko wanne lokaci 'yan takara kan dauki alkawurika.Ko shekaru nawa wadanda ake zabe ke bukata don cika alkawuran da suka dauka?wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
-
939
Gaskiyar Tasirin Amfani Da Irin Noma Da Aka Canzawa Halitta GMO
Send us Fan MailAlamu na nuna cewa galibin manoma a Najeriya suna da shakku a kan amfani da irin da aka sauya ƙwayoyin halittarsa.Hakan dai na faruwa ne duk da bayanan da wasu masana suka yi game da alfanun wannan iri wanda ake kira GMO ko Genetically Modified Organism a turance.Tuni dai wasu masanan, waɗanda suka shirya wani taron bita ga manema labarai, suka yi gargaɗi game da illolin irin.Ko mece ce gaskiya game da amfani da wannan iri na GMO?
-
938
Shin Ya Kamata A Samar Da Dokokin Da Za Su Sa Ido Kan Amfani Da AI?
Send us Fan MailTun bayan bayyanar kirkirarrriyar basira wato AI ne dai wasu mutane suke amfani da ita ta hanyar da da bai kamata ba. Wasu sukan yi amfani da ita wajen saka hoto ko kirkirar faifan bidiyo wanda zai nuna wani yana yin abun da bai kamata ba. Hakan dai ya sa wasu suna ganin ya kamata a samar da dokokin da za su rinka lura da yadda ake amfani da kirkirarriyar basirar. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan dacewar sanya doka gane da yadda mutane za su rinka amfani da fasahar AI.
-
937
Yadda Masu Yi Wa Kasa Hidima Za Su Ci Arzikin Yankunan Da Suke AIki
Send us Fan MailBayan hadin kai da karfafa fahimtar juna wadanda hidimar kasa take kawowa, akan samu wasu masu hidimar da sukan yi amfani da duk wata dama da suka samu don neman na sakawa a bakin salati. Yayin da wasu masu hidimar kasa sukan kama sana’a ko su saka hannun jari a inda aka tura su, wasu kuwa komawa garuruwansu suke yi bayan sun kammala. Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan irin damar da masu yi wa kasa hidima suke da ita a garuruwan da aka tura su.
-
936
Yadda Matasa Ke Bada Gudunmawar Cigaban Al’ummarsu
Send us Fan MailSamun matasan dake bada gudunmawa a alummomin da suke rayuwa a cikin ta yana da matukar wuya a wannan zamani. Amma duk da haka, wasu matasa sun sadaukar da rayuwarsu wajen bada gudunmawarsu wajen cigaban alummarsu. Shirin Najeirya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan irin gudunmawar da matasa ke badawa wajen cigaban alummarsu
-
935
Yadda Na Rasa 'Ya'ya Na Ga Guban Abinci
Send us Fan MailCin guba ta hanyar abinci (food poisoning) wata cuta ce da ke faruwa idan mutum ya ci abinci ko ya sha abin sha da ya gurɓace. Gurɓacewar abincin na iya fitowa daga ƙwayoyin cuta kamar Salmonella, E. coli, ko Listeria, ko kuma daga ƙwayoyin cutar virus, ƙwari (parasites), ko sinadarai masu guba. Alamomin cutar sun haɗa da ciwon ciki, amai, zazzabi, gudawa, da rashin jin daɗin jiki. A wasu lokuta masu tsanani, cutar na iya kai mutum asibiti ko ta yi barazana ga rayuwa, musamman ga yara ƙanana, mata masu ciki, tsofaffi, da masu raunin garkuwar jiki. wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba akai.
-
934
Daga Alkawari Zuwa Mulki, Yadda Siyasa Ke Sauya Manufa
Send us Fan MailDuk bayan shekaru hudu, Najeriya na kara yin zabe kuma ko wanne lokaci 'yan takara kan dauki alkawurika.Ko shekaru nawa wadanda ake zabe ke bukata don cika alkawuran da suka dauka?wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
-
933
Abubuwan Da Za Su Kwadaita Muku Azumtar Sitta Shawwal
Send us Fan MailAlqurani mai girma a cikin suratul Baqarah Allah ya wajabta wa musulmi da suka cika wasu sharudda azumtar watan Ramadana.Kamar yadda malamai suka sha fadi, wannan wata na dauke da wasu falala maras misaltuwa da bawa kan samu idan ya maida kai wajen ibada don samun rabauta daga ubangiji.Kazalika hadisai sun ruwaito kan falalar azumtar kwanaki shidda na watan shawwal, watan dake biye da Ramadan.Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan falalar dake akwai ga wanda ya azumci kwanaki shidda na watan shawwal.
-
932
Azumin Ramadana: Ko Kun San Dabinon Da Kuke Shan Ruwa Da Shi?
Send us Fan MailKo kun san sunan dabinon da kuka fi so ku ci a lokacin shan ruwa? Dan Agadas ne, ko Ruwa-Ruwa, ko Annakhiyl? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai ya yi nazari ne kan nau’ukan dabino da alfanunsa ga dan’Adam, musamman mai azumi.
-
931
Kalubalen Dake Tattare Da Samar Da ‘Yansandan Jihohi A Najeriya
Send us Fan MailShugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya sha nanata muhimmancin samar da ’yan sandan jihohi a Nigeria, yana mai cewa hakan na daga cikin hanyoyin da za su taimaka wajen magance matsalolin tsaro da ke addabar sassa daban-daban na kasar. Shugaban ya bayyana cewa tsarin ’yan sanda da ke karkashin gwamnatin tarayya kadai ba zai iya biyan bukatun tsaro na kasa mai yawan jama’a da fadi kamar Najeriya ba.A wani mataki na ci gaba da duba yiwuwar aiwatar da wannan tsari, Sufeto Janar na ’Yan Sandan Najeriya, Tunji Disu, jim kadan bayan kama aikinsa ne ya kafa wani kwamiti na musamman domin nazartar hanyoyin da za a bi wajen samar da ’yan sandan jihohi.Sai dai duk da yadda wasu ke ganin cewa kafa ’yan sandan jihohi zai taimaka wajen inganta tsaro, masana da masu ruwa da tsaki na cewa akwai kalubale da dama da ka iya tasowa.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan irin kalubalen da shirin samar da ‘yansandan jihohi zai iya fuskanta.
-
930
Yadda Cutar Zazzabin Lassa Ke Kisa Da Hanyoyin dakile Ta
Send us Fan MailA yayin da Najeriya ke fuskantar kalubale daban-daban a fannin lafiya, cutar zazzabin Lassa ta sake ɗaga kai a wasu jihohin ƙasar. Cutar wadda ake dangantawa da berayen da ke ɗauke da ƙwayar cutar, tana yawaita ne musamman a lokutan sanyi zuwa farkon damina, lamarin da ke jefa al’umma cikin fargaba a kowace shekara.Rahotanni daga hukumar dake hana yaduwar cututtuka ta Najeriya sun nuna cewa tun daga farkon shekarar 2026, an samu daruruwan mutane da suka kamu da cutar a jihohi fiye da goma sha huɗu, tare da mace-mace da dama. Jihohi irin su Bauchi State, Ondo State, Taraba State da Edo State na daga cikin wuraren da cutar ta fi yin kamari.Idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata, alkaluma sun nuna cewa 2025 ta samu yawan masu kamuwa da cutar fiye da yadda aka fara gani a 2026, sai dai masana sun nuna damuwa kan yadda mace-mace ke iya ƙaruwa sakamakon jinkirin kai marasa lafiya asibiti.Shin me ke haddasa wannan yawaitar a kowace shekara? Wadanne hanyoyi za a bi wajen magance ta?Wadannan da ma wasu tambayoyin shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi kokarin amsawa.
-
929
Yadda Ake Kamuwa Da Basir Da Hanyoyin Magance Ta
Send us Fan MailCutar basir na daga cikin cututtukan da mutane da dama ke da mabanbantan ra’ayoyi akan ta.A lokuta da dama za ka ji yadda mutane ke fadin dalilai daban daban da ke janyo cutar basir, yayin da wasu ke ganin yawan zama ne ke kawo ta, wasu kuwa gani suke yi zaki da maiko ne ke kawo ta.Wannan shine abun da da yawa daga cikin mutane suka sani kan wannan cuta, sai dai masana kiwon lafiya na da nasu fahimtar daban kan wannan cuta.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai tattauna ne kan cutar basir da hanyoyin magance ta.
-
928
Yadda Azumi Ke Inganta Lafiyar Jiki
Send us Fan MailAlumma na yin azumi ne bisa dalilan addini don samun lada kamar yadda Allah ya umurta a cikin Qurani mai girma. Sai dai daga baya binciken masana kimiyya ya gano cewa bayan lada da ake samu daga yin azumi, akwai wasu alfanu da mai azumi ke samu ga lafiyar jikin shi da suka hada da inganta karfi da zurfin tunani zuwa fitar da gurbatattun abubuwa da jiki baya bukata. A takaice dai, ba kawai lada mai azumi ke samu ba, har da samun lafiyar jiki da na kwakwalwar sa. Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi Nazari ne kan alakar dake akwai tsakanin yin azumi da kuma lafiyar jikin mutum.
-
927
Falalar Bude Baki Cikin Iyali A Lokacin Azumi
Send us Fan MailHadisi ya tabbatar da yadda cin abinci tare yake kara dankon zumunci da kaunar juna da albarka a tsakanin al’umma. Mai yiwuwa wannan ne ya sa akan samu Karin kusanci da shakuwa a tsakanin duk iyalan da kan zauna su ci abinci. Ko kafin watan azumi dai, wasu magidantan kan mayar da cin abinci tare da tare da iyalin su al’ada. Shin ko mene ne matsayin bude-baki tare da iyali a watan Ramadana? Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan irin alfanun da bude baki tare da iyali yake da shi.
-
926
Me Nadin Sabon Sufeton 'Yansanda Ke Nufi Ga Tsaron Cikin Gida Najeriya?
Send us Fan MailShugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa sabon Sufeto Janar na ‘Yan Sanda (IGP), matakin da ya sake jawo hankalin al’umma kan makomar tsaro da gyaran harkokin rundunar ‘yan sandan ƙasar nan. Naɗin sabon jagoran rundunar ya zo ne a daidai lokacin da ake fuskantar ƙalubale daban-daban na tsaro, ciki har da satar mutane, ta’addanci, da rikice-rikicen cikin gida a wasu sassan ƙasa.Sabon Sufeton ana sa ran zai ɗora kan nasarorin da aka samu a baya tare da kawo sababbin tsare-tsare da dabarun da za su ƙarfafa yaƙi da laifuka, inganta hulɗa tsakanin ‘yan sanda da al’umma, da kuma farfaɗo da martabar rundunar. Ko ta yaya wannan naɗin sabon shugaban ‘yansandan zai amfani tsaron cikin gida Najeriya?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
-
925
Shin Da Gaske An Fara Samun Ɓaraka Tsakanin Atiku Abubakar Da Peter Obi A Tafiyar ADC?
Send us Fan MailRahotanni daga sassa daban-daban na siyasar Najeriya na nuna cewa ana fara samun ɓaraka a tsakanin manyan jiga-jigan haɗakar tafiyar ADC, musamman tsakanin tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da kuma tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party, Peter Obi.Ko da yake har yanzu babu wata sanarwa ta hukuma da ke tabbatar da wannan saɓani, majiyoyi na nuni da cewa sabanin ra’ayi kan jagoranci, tsarin tafiya, da kuma makomar zaɓen 2027 na iya zama tushen wannan rikici.Wasu masu sharhi na ganin cewa irin wannan saɓani abu ne da kan taso a duk wata haɗaka ta siyasa, musamman idan manyan ‘yan takara masu farin jini suna ƙoƙarin haɗa kai domin cimma buri ɗaya. Sai dai tambayar ita ce: shin wannan ɓaraka za ta iya raunana haɗakar kafin ta kai ga gaci, ko kuwa za a samu sulhu a tsakaninsu?A yau, shirin Najeriya A Yau zai yi duba ne kan gaskiyar lamarin, me ke haddasa wannan jita-jita, da kuma irin tasirin da hakan zai iya yi ga makomar siyasar Najeriya.
-
924
Falalar Sallan Tarawih Ga Alummar Musulmi A Watan Ramadan
Send us Fan MailA duk lokacin da watan azumin Ramadan ya kama, al’ummar Musulmi kan cika masallatai domin gudanar da sallar Tarawihi cikin karsashi da himma. A kwanakin farko, ana ganin sahu sun cika, zuciya cike da nishadi da kwadayin lada. Sai dai abin takaici, bayan wasu kwanaki, wasu kan fara ja da baya — wani saboda gajiya, wani saboda shagaltuwa da harkokin yau da kullum, ko kuma rashin juriya.Wannan yanayi na nuna bukatar tunatarwa kan muhimmanci da falalar sallar Tarawihi, domin ita ba kawai karin ibada ba ce a watan Ramadan, illa wata babbar hanya ce ta neman gafara da kusanci ga Allah. Manzon Allah (SAW) ya karfafa tsayuwar dare a watan Ramadan, yana mai bayyana cewa duk wanda ya tsaya sallar dare cikin imani da neman lada, za a gafarta masa zunubansa na baya.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai duba ne kan falalar sallan tarawihi yayin da Musulmi ke cigaba da gudanar da azumin watan Ramadan.
-
923
Dalilan Kamuwa Da Cutar Hawan Jini Da Hanyoyin Magance Ta
Send us Fan MailCututtuka da dama suna Kamari a Najeriya wanda a mafi yawancin lokuta ma wadanda ke dauke da irin wadannan cututtukan basu da masaniyar suna dauke da su. Kamar yadda majalisar dinkin duniya ta bayyana, zaman lafiya, rashin matsalar kwakwalwa, da samun wadata na daga cikin abubuwan dake tabbatar da lafiyar bil’adama. Wata cuta da ta addabi da yawa daga cikin al’umma itace cutar Hawan jini wacce take daya daga cututtuakan dake sanadiyyar mutuwar akalla mutum miliyan biyu a duk shekara a Najeriya.
-
922
Yadda Masu Larurar Ulcer Za Su Gudanar Da Azumin Ramadan Ba Tare Da Matsala Ba
Send us Fan MailA duk lokacin da watan azumi ya zo, Musulmai da dama sukan karɓe shi da murna da shauƙi, suna shirya ibada da ƙara kusanci da Allah. Sai dai ga wasu, musamman masu fama da larurar gyambon ciki wato ulcer, watan azumi kan zo da wani yanayi na damuwa da fargaba. Yayin da wasu ke jin daɗin azumi, su kuma suna cikin ƙalubalen yadda za su iya jure yunwa da ƙishirwa ba tare da cutar ta tashi ko ta jawo musu matsananciyar wahala ba.Ciwon ulcer na haddasa zafi a ciki, tashin zuciya, amai ko jin ƙuna musamman idan ciki babu komai na tsawon lokaci. Wannan ne ya sa azumi, wanda ke buƙatar jure yunwa daga asuba zuwa magariba, kan zama babban ƙalubale ga masu fama da wannan larura. Wasu kan kasa yin azumi gaba ɗaya, yayin da wasu ke fara shi amma su kasa kammalawa saboda tsananin ciwo.Ko ta wadanne hanyoyi ne masu fama da wannan larurar zasu bi wajen yin azumi ba tare da sun sha wahala ba?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau zai yi duba a kai.
-
921
Yadda Muka Yi Asarar Miliyoyin Naira A Kasuwar Singa Muna Ji Muna Gani
Send us Fan Mail‘Yan kasuwa da dama a jihar Kano sun kwana sun tashi da juyayi da alhinin gobara da ta faru ta kuma lashe musu dimbin dukiyarsu suna ji suna gani ba tare da sun iya tabuka komai ba.Gobarar da ta tashi a kasuwar singa dake jihar Kano, ta fara ne da misalin karfe 4:30 na ranar asabar ta kuma cigaba da ci har zuwa wayewar garin ranar lahadi. Wannan gobara ta yi sanadiyyar raba ‘yan kasuwa da dama da hanyar cin abincin su, inda ta jefa su da iyalansu cikin halin kunci.Ko wanne irin hasara wadannan ‘yan kasuwa suka tafka sakamakon wannan gobara?Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai.
-
920
Ya Kamata Najeriya Ta Samar da Dokoki Kan Amfani da AI?
Send us Fan MailTun bayan bayyanar kirkirarrriyar basira wato AI ne dai wasu mutane suke amfani da ita ta hanyar da da bai kamata ba. Wasu sukan yi amfani da ita wajen saka hoto ko kirkirar faifan bidiyo wanda zai nuna wani yana yin abun da bai kamata ba. Hakan dai ya sa wasu suna ganin ya kamata a samar da dokokin da za su rinka lura da yadda ake amfani da kirkirarriyar basirar. Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan dacewar sanya doka game da yadda mutane za su rinka amfani da fasahar AI.
-
919
Hanyoyin Magance Laifukan Da Matasa Ke Aikatawa A Cikin Al'umma
Send us Fan MailMasu iya magana kan ce banza ba ta kai zomo kasuwa. In ba haka ba, me ya kai matasan da ake zargi da aikata manyan laifuffuka ofishin ’yan sanda, suka kuma fit oba tare da wani ya harae su ko ya yi mutsu tsawa ba, balle ya saka su a cell? ’Yan sandan dai sun ce wannan wata dabara ce ta yakar aikata manyan laifuka irin su sata da fashi da makami da kwacen waya da fyade kai har ma da satar mutane don kudin fansa a tsakanin matasa.Ko yaya wannan dabara take aiki? Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari a kai.
-
918
Abin Da Ya Sa ’Yan Najeriya Ba Sa Samun Wadataccen Abinci
Send us Fan MailA wannan zamani, ’yan Najeriya da dama ba sa samun wadataccen abinci a yini.Magidanta da dama, musamman, sun tsallake sun bar iyalansu sun shiga bariki don neman na sanyawa a bakin salati. Mene ne dalilin hakan, kuma yaya za a yi a kauce wa fadawa cikin irin wannan yanayi? Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan halin da galibin ’yan Najeriya suka tsinci kansu a ciki na rashin samun abinci yadda ya kamata
-
917
Dabarun Bunkasa Kasuwanci A Intanet
Send us Fan MailMasu iya magana kan ce “zamani riga”.Sauyin zamani ya kawo sauye-sauye da dama a yadda ake gudanar da harkoki, ciki har da kasuwanci.A yanzu haka, zamani, intanet na taka muhimmiyar rawa wajen tallata haja ko saye da sayarwa.Shrin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan dabarun da za ku iya amfani da su don bunkasa kasuwancinku ta hanyar amfani da intanet.
-
916
Tasirin Yankan Al’aura A Rayuwar 'Ya'ya Mata
Send us Fan MailA tsakanin al’ummomi daban-daban akan samu wasu al’adu na yanke wani bangare na al’aurar ’ya’ya mata saboda wasu dalilai.A kasar Hausa akan yi abin da ake kira yankan angurya da nufin rage wa mace sha’awa, musamman kafin ta yi aure.Ko menene tasirin wannan al’ada a rayuwar ’ya’ya mata?Albarkacin Ranar Yaki da Yankan Al’aurar Mata ta Duniya, shirin Najeriya A Yau zai yi nazari a kan wannan batu.
-
915
Hanyoyin Mallakar Gida Ga Mai Karamin Karfi
Send us Fan MailMallakar muhalli na cikin burace-buracen kusan kowanne dan Najeriya.Sai dai wadannan burace-burace, a galibin lokuta, ba sa cika – musamman ga masu matsakaitan samu.Amma wasu masana suna ganin akwai dabarun da marasa karfi ma za su iya amfani da su don su mallaki nasu muhallin, daidai ruwa daidai tsaki.A kan wadannan dabaru shirin Najeriya A Yau zai yi nazari..
-
914
Abin Da Ya Kamata Ku Yi Yayin Takaddama Da ’Yan Sanda
Send us Fan MailBabban alhakin da Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya dora wa Rundunar ’Yan Sanda shi ne kare rayuka da dukiyoyin ’yan kasa. Sai dai a lokuta da dama, akan samu fito-na-fito sakamakon zargin ’yan sanda da wuce gona da iri wajen gudanar da aiyyukan nasu.Shirin Najeriya a Yau ya tattauna a kan yadda abubuwan da ya kamata ’yan kasa su yi idan ’yan sanda suka nemi cin zalinsu.
-
913
Rayuwar Mazan Da Ba Sa Haihuwa
Send us Fan MailRashin haihuwa matsala ce da ka iya wargaza gidajen aure musamman a wannan zamani.Da an samu shekara biyu zuwa uku bayan an daura aure ba tare da an samu karuwa ba za a fara yamadidi da matar a kan ba ta haihuwa.Sai dai likitoci sun ce maza ma ka iya fama da wannan larura saboda wasu dalilai.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan wadannan matsalolin da suke hana maza haihuwa.
-
912
Radadin da masu amosanin jini suke sha
Send us Fan Mail
-
911
Inda Aka Mike Da Inda Aka Kauce Tun Bayan Dawowa Mulkin Dimokuraɗiyya A Jamhuriya Ta Hudu
Send us Fan MailKamfanin yaɗa labarai na Media Trust ya daɗe yana taka muhimmiyar rawa wajen buɗe tattaunawa masu ma’ana kan manyan al’amuran da suka shafi tafiyar da ƙasa da dimokuraɗiyya a Najeriya. Daga cikin fitattun shirye-shiryensa akwai muhawarar shekara-shekara da kamfanin ke shirya wa, wadda ta zama wani dandali na musamman da ke haɗa masana, ‘yan siyasa, masana doka, da masu ruwa da tsaki domin nazari da tantance halin da ƙasa ke ciki.A bana, wannan muhawara ta kai karo na 23, inda aka zaɓi mayar da hankali kan abin da aka yi daidai da kuma abin da aka kasa yi tun bayan dawowar Najeriya mulkin farar hula a jamhuriya ta huɗu.Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci, ya duba sama da shekaru ashirin na tafiyar dimokuraɗiyya, wadanne irin nasarori ko akasin haka aka samu? Shin ko Najeriya ta kai ga ci a kokarinta na cimma muradun dubban yan kasa?
-
910
Tasirin Siyasar Matasa A Najeriya Tun Bayan Dawowar Jamhuriya Ta Hudu
Send us Fan MailShekaru kafin a sanya hannu kan dokar Not Too Young To Run, siyasar matasa a Najeriya na fuskantar ƙalubale masu tarin yawa. Duk da cewa matasa su ne mafi rinjaye a yawan al’umma da kuma masu katin zaɓe, an dade ana kallonsu ne a matsayin masu ɗaukar tutoci, da yaɗa saƙonni ko kuma masu tayar da tarzoma a lokacin zaɓe, ba tare da ba su cikakkiyar dama ta tsayawa takara ko shiga manyan matakan yanke shawara ba.Sai dai a shekarar 2018, bayan sa hannu kan dokar bai wa matasa dama a siyasar Najeriya, an samu sabon salo da fata a fagen siyasa. Dokar ta rage shekarun tsayawa takara a muƙaman siyasa daban-daban, tare da buɗe ƙofa ga matasa masu ƙwazo, da ilimi da kishin ƙasa su shiga fafutukar jagoranci kai tsaye. Wannan mataki ya ƙarfafa gwiwar matasa da dama su fara ganin siyasa a matsayin fagen da za su iya kawo sauyi, ba wai kawai a matsayin masu goyon baya ba.-A cigaba da kawo muku shirye gabanin muhawarar Daily Trust, shirin Njaeriya a yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan ko yadda siyasar matasa ta kasance a jamhuriya ta hudu tun bayan ayyana wannan doka.
-
909
Yadda Siyasar Ubangida Ta Yi Tasiri Ga Siyasar Najeriya A Jamhuriya Ta Hudu
Send us Fan MailTun bayan dawowar mulkin farar hula a shekarar 1999, siyasar Najeriya ta kasance karkashin inuwar wasu ’yan tsiraru da ake kira iyayen gidan siyasa. Wannan tsari ya ginu ne a kan karfin mutum guda ko rukuni, inda su ke rike da makullin jam’iyya, su tsara wa’adi, su zabi ’yan takara, su kuma yanke hukunci ba tare da la’akari da ra’ayin mafi yawan mambobi ko jama’a ba.A Jamhuriya ta Hudu, siyasar ubangida ta zama tamkar al’ada da aka amince da ita, inda dimokuraɗiyya ta hakika ke fuskantar barazana daga siyasar biyayya da ladar mukami. A maimakon gasa ta tunani, da tsari da manufofi, an koma fafatawa ta kusanci da ubangida, wanda hakan ya raunana jam’iyyu, ya haifar da rikice-rikicen cikin gida, tare da jefa talakawa cikin rashin tabbas game da sahihancin zabensu.A cigaba da kawo muku shirye shirye gabanin Muhawarar Daily Trust ta 2025, shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba ne kan Siyasar Uban gida ya yi tasiri da kuma yadda ya juya akalan siyasar Najeriya tun dawowar jamhuriya ta hudu a Najeriya.
We're indexing this podcast's transcripts for the first time — this can take a minute or two. We'll show results as soon as they're ready.
No matches for "" in this podcast's transcripts.
No topics indexed yet for this podcast.
Loading reviews...
ABOUT THIS SHOW
Shiri ne na minti 15 dake duba na tsanaki, da nazari mai gamsarwa, tare da tsokaci mai amfanarwa, a kan batutuwan da ke ɗaukar hankali a lamuran yau da kullum.
CATEGORIES
Loading similar podcasts...